Dahiru Bauchi ya yi magana kan raba masarautar Kano
Latsa hoton da ke sama don kallon bidiyon
Shahararren malamin addinin Musulunci a Najeriya, Sheikh Dahiru Bauchi ya yi wa BBC karin bayani dangane da ra'ayinsa a kan rarraba masarautar Kano.
Ya bayyana cewa ko Turawan mulkin mallaka ba su rarraba masarautun Kano ba, kamar yadda gwamnatin Kano ta yi a wannan lokaci.
Ya kuma yi karin bayani game da harkokin tsaro da halin da mutane suka tsinci kansu a Najeriya.