Dalilin da ya sa muka sauya kasafin kudi - Namdas
Majalisar dokokin Najeriya ta mayar da martani game da korafin da Shugaban kasar Muhammadu Buhari ya yi a kan cewa bangaren ya yi masa cushe a cikin kasafin kudin da ya mika masa.
Shugaban kwamitin watsa labarai na majalisar, Abdulrazak Namdas, ya ce daya daga cikin dalilan da suka sa majalisar ta rage kudaden da za a saka a wasu ayyuka shi ne ganin cewa ba lallai ba ne a iya amfani da kudaden da aka fitar wa ayyukan cikin shekara daya ba.