Hotunan ganawar Osinbajo da shugabannin Igbo

A ranar Laraba ne mukaddashin shugaban Najeirya Yemi Osinbajo ya gana da shugabannin al'ummar Igbo a fadar gwamnati a Abuja, to ko me ya gaya musu?

Osinbajo da shugabannin Igbo

Asalin hoton, Presidency

Bayanan hoto, A ci gaba da ganawarsa da shugabannin al-umma daga sassa daban-daban na Najeriya kan yadda za a magance matsalar kalaman kiyayya, mukaddashin shugaban Najeriya, Farfesa Yemi Osinbajo, ya gana da shugabannin al'umma daga yankin Kudu maso gabashin kasar a ranar Laraba.
Osinbajo da shugabannin Igbo

Asalin hoton, Presidency

Bayanan hoto, Osinbajo ya ce tashin hankali da yaki ba zai taimaka wa kowa ba, saboda shi yaki yana da saukin farawa amma da wahala a gama shi har abada.
Osinbajo da shugabannin Igbo

Asalin hoton, Presidency

Bayanan hoto, Osinbajo ya ce dole shuwagabannin su fito su yi tir da kalaman kiyayya da ke faruwa tsakanin al'ummominsu.
Osinbajo da shugabannin Igbo

Asalin hoton, Sunday_Aghaeze@ 2017

Bayanan hoto, Mukaddashin shugaban Najeriyar ya ce babu shakka game da kudurin gwamnati na hukunta duka masu kalaman kiyayya da rarrabuwar kai.
Osinbajo da shugabannin Igbo

Asalin hoton, Sunday_Aghaeze@ 2017

Bayanan hoto, Farfesa Osinbajo ya ce wannan ba lokacin da za a buya karkashin kabila ko addini ba wajen nuna goyon baya ga kalaman da ke rarraba kawunan al'umma.
Osinbajo da shugabannin Igbo

Asalin hoton, Sunday_Aghaeze@ 2017

Bayanan hoto, Taron ya samu halartar shuwagabanni daga yankin kudu maso gabashin kasar da kuma manyan jami'an gwamnati.
Osinbajo da shugabannin Igbo

Asalin hoton, Sunday_Aghaeze@ 2017

Bayanan hoto, Ba a bar mata a baya ba a cikin mahalarta taron, kuma Farfesa Osinbajo ya ce a ranar Litinin zai gana da dukkan shugabannin addinai da manyan kabilun kasar.
Osinbajo da shugabannin Igbo

Asalin hoton, Sunday_Aghaeze@ 2017

Bayanan hoto, Shuwagabbin majalisar dokokin Najeriya ma sun halarci zaman taron.
Osinbajo da shugabannin Igbo

Asalin hoton, Sunday_Aghaeze@ 2017

Bayanan hoto, Taron na zuwa ne a daidai lokacin da ce-ce-ku-ce ke dada kamari dangane da fafatukar kafa kasar Biafra da wasu 'yan kudu maso gabashin kasar ke yi.
Osinbajo da shugabannin Igbo

Asalin hoton, Sunday_Aghaeze@ 2017

Bayanan hoto, Mukaddashin shugaban Najeriya ya bayyana wa shuwagabannin yankin bukatar da ke akwai na wanzuwar zaman lafiya da hadin kai a Najeriya.