Gane Mini Hanya
Gane Mini Hanya
Najeriya na daga cikin ƙasashen da rahotoni suka bayyana a matsayin ɗaya daga cikin ƙasashen da ke fuskantar barazana ta fuskar ‘yancin faɗar albarkacin baki a fadin duniya.
Sau da yawa aka zargi mahukunta a ɓangarori da dama game da kamawa da tsarewa, ko ma rufe wasu kafofin yaɗa labarai, saboda wasu dalilai masu alaƙa da saɓa ƙa’idar aiki, kodayake wasu na zargin cewa bi-ta-da-ƙulli ne kawai, don hana ‘yancin faɗar albarkacin baki.
Yayin wata ziyara da ya kawo ofishin BBC da ke Landan, shugaban hukumar kula da kafofin yaɗa labaran ƙasar NBC Balarabe Shehu Illela ya ce babu ƙamshin gaskiya a wannan zargi.
Ga kuma tattaunawarsu da Imam Saleh