Gane Mini Hanya: Tare da ministan tsaron Najeriya Badaru Abubakar

Bayanan sautiLatsa hoton sama don sauraron shirin
Gane Mini Hanya: Tare da ministan tsaron Najeriya Badaru Abubakar

Gwamnatin Najeriya ta jaddada cewa ana samun gagarumar nasara a yaki da matsalolin tsaron da suka addabi ƙasar.

Wannan na zuwa ne yayin da gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ta lashi takobin magance matsalar yayin da ta cika shekara biyu a kan Mulki.

Sai dai duk da iƙirarin gwamnatin, har yanzu ana samun rahotannin kai hare-hare a sassa daban-daban na ƙasar da ke fama da wannan matsala, lamarin da ya janyo mutuwar mutane fiye da17,000 a cikin waɗannan shekaru biyu, a cewar alkaluman kamfanin tsaro na Beacon Consulting.

A filinmu na Gane Mani Hanya na yau, Imam Saleh ya tattauna da ministan tsaron Najeriyar, Muhammad Badaru Abubakar, wanda ya fara da yin bayani a kan yadda suka tunkari matsalar, bayan sun karɓi mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.